XtGem Forum catalog
Home
BARKA DA ZUWA
SHAFIN LIATTAFAN YAKI

public public

yayana mijina

yayana mijina
YAYANA MIJINA Part 1-10 , Sarah ki rike mutincin ki na diya Mace bawai zamu tura ki makaranta dan ki dinga abin da kika ga dama bane, aa kawai dan muna so ki kara karatun ki kafin yayan ki Ya dawo sannan ina san kisa a ranki kefa matar aure ce ke matar wani ce banda kula mutanen banza danda biyewa professor ki kare mutunciki na diya mace kuma mai aure, ina fatan kin fa himta? Na fahimta baba, amma baba wannan wanne irin mijine ban taba ganiba bai taba ganina ba, murmushi yaii sarah kenan kawai inasan kisa a ranki mujinki yayanki, komai dan lokacine kina zaune wataran zakiga ko waye mujin ki dai kawai ki Kare mutun cin ki, insha Allahu baba, Allah yai miki albarka, ameen baba, gode da wuri zaku wuce kaduna saboda haka kije ki kwanta kiyi bacci da wuri dan ki sami tashi da wuri, shikenan babaa,. Wani daki stair naga ta nufa tabi wani daki, wata mata na xaune da newspaper a hannun ta, mama sannu da aiki, yauwa yar ta har kun gamaa magana da Baban naki,? eh mama, sarah inasan kibi maganar mahaifin ki duk da nasan gidan da zaki yanzu bawai wani dadin zama zakiji da su ba aamma ki daure jara bawace Allah Ya kaddara miki,. Mama meyasa kika ce haka, sarah bari yau zan vaki labarin family dinmu yau xakiji komai yau zan sanar miki ko wace hajiya luba,. Shekaru asirin da suka wuce,. . Shekaru ashrin da suka wuce, a zahirin dangin mu ka,idace sai anwa mutun hadin gida wannan abu tun daga kakanni ne, haka muka taso muka gani ana yi, da lubabu dani Zainab uban mu daya uwa kuwa da tashi,mafiyar mu hadin gida aka mata da mahaifin mu,sunyi shekara ammaaa vabu alamar haihuwa sunje asibi aka saida musu baza ta taba haihuwa Ba hakan Ya tada da hankalinta sosai, dole tasa babanmu Ya karo aure, wacce ba dangi ba,amma kwata kwata jinin harira amaryar babanmu bai hadu dana umma Ba kwata kwata ta tsane ta kuma ba dalili,. Kuma hakan yana batawa baba raii amma umma ta nuna ba wani abu, Umma itta kadaice a gun mahaifanta, baban kuma Dan gidan yayan Baban mu ne, haka suke rayuwa tashi daya Allah yaba harira ciki, ba karamin murna mukai ba nina,haka akai ta kula da ciki har yakai haihuwa,ranar hai huwa ta haifi diya mace, ranar suna taci suna LUBABATU,habaici umma tasha ranar hakan yasa zazzabi da alhaji yaji taba da lafiya Ya kaita asibiti nan ake shida masa tna ciki basuyi wani mamaki ba tunda kanyin yadda yaso,. Umma ranar haihuwa ta haifu ni, ranar suna naci sunan Zainab abu sosai akai shagali haka bba yai ta kula damu cikin jin dadi da godewa Allah,. Har muka girma aka samu makaranta amma lubabatu halin maman ta taiyi, kullun cikin nuna bakin ciki da kwashi, haka mukai ta rayuwa har Allah yayi muka kai mum zalin aure nan aka Tara family aka za,a hadani aure da mahaifin ku wato Aminu, lubabatu kuma da yakubutu duk yayan yayan babanme, amma me haka lubabatu ta dire itta aminu take so inda Yan uwa sukace ba wanda Ya isa sa su canza shawara, tun daga ranar tsana ta shiga tsakanin mu sosai har akai aure,. Cikin idon Allah har shekara biyar ban sami haihuwa ba, kuma ko a jikin alhaji, a lokacin lubabatu ta haifi danta Na miji wato *ashrim* ran suna munsha guri wai dama dole inyi gado niko ko a jikina tun mijina bai damuba Maye nawa Na damuwa,. Haka rayuwa ta ci gaba . Har shekra 7ba haihuwa nan nada da hankali sai munje asibiti,muna zuwa kai mun aune aune nan aka sanar ina dauke da ciki wata biyu, abin yaban mamaki ko irin wannan abun da akeji ni banji ba, haka muka dawo jida cikin murna, lokacin lubabatu yayanta biyu dan ittama ta daina haihuwa bisa wasu dalilai, lokacin da ashrin yayi wayo babanshi waje Ya fitar dashi karatu Dan kuwa family dinmu Allah yai musu arziki,. Ranar da zan haihu aka kaini asibiti nasha wuya daga baya Na haifu ki, ranar suna kikace sunan Mamana, wato Aisha akan yasa muke kiranki da sarah, haka kika taso cikin kulawa, har kikai wayo muka saki makaranta, har Allah yayi gashi kin kammala, tashi daya kuma aka yanke hukuncin hada ki aure da ashrim ba yadda Na iya dole Na hakura, yanzu baxan iya gane ashrim ba ya yake ina yake ya dabi arshi take, duk ban sani ba, Amman ina mai baki hakuri akan ki kula da mujin kibi umarnin iyaye,. Sauke ajiyar zuciya tare da fadin insha allahu, . Haka ta nufi dakinta jiki a sanyaye,. .
Back to posts